Connect with us

Labarai

ƁANGAREN JAWABIN JAGORA SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H) KAN GWAGWARMAYAR IMAM KHOMEINI (QS)

Published

on

“Har ma an ce wani lokaci wadansu daga cikin mabiya Imam sun ga kisan da Shah yake yi ya yi yawa, suka je suka samu Imam, suka ce Ya Imam, mutumin nan fa kisan da yake yi zai iya karisar da al’umma. Ba yadda za a yi a dan sassauta? Kisan fa ya yi tsanani.

Suna yin wannan maganar, sai Imam yace musu su kawo masa ‘list’ na mutanen da za su iya gudanar da Gwamnati in an kafa. Su suna kokarin yadda za a sassauto, shi kuma ga matakin da ya je. Yace musu wannan al’amari na Allah ne, kuma zai tabbatar da shi.

Ka ga wannan al’amari irin na Imam Malam. Tsayuwa Kyam! Shima Genaral Huyser a cikin littafinsa yake cewa; Kuma sai su ga mutumin nan ya dauki wani ‘dangerous step’ wanda ba yadda za a yi mutum ya dauki wannan ya yi nasara, amma shi sai ya yi nasara.

Alal misali, su soja suna harbin mutane. Abin da aka saba ‘normally’ idan wasu suka zo suna harbinku, ku ma dole ku samu ko da duwatsu ne ku harbe su ko? To shi Imam sai yace a’a, a basu ‘flower’ ne. Shi kuma flower yana da daraja a wajen mutumin Iran, mu nan bamu san ma’anar flower ba, amma ‘yan Iran sun sani…..

Cikin ‘slogans’ din (mabiya Imam) har da cewa “Haba sojojinmu, me yasa kuke harbinmu? Haba sojojinmu, me yasa kuke kashemu?” Shi kuma Imam (QS) ya yi jawabi, a ciki yake cewa: “Haba soja, in ka yarda ka zama bawan wasu, maimakon ka yi wa kasarka hidima? Yanzu mutanenka za ka kashe maimakon ka yi musu aiki?” Imam yace: “Ka yar musu da ‘uniform’ dinsu, ka bar masa barikin, gudu kawai ka koma kauyenku.”

To, su ba su dauka soja zai ji wannan maganar ba. Sai kawai sojoji suka fara daina harbin. In an turo su aiki, sai kawai su yar da ‘uniform’ su bi mutane kawai. In an dora kamar soja 600 su je, in aka dawo sai a ce kamar soji 50 ba su dawo ba. in aka sake zuwa kuma sai a ce yanzu kuma 100 ba su dawo ba.

Sai suka fara cewa to yadda za a yi yanzu, da yake ba sa saka hula, da wuyar gaske ka ga hula a kan mutanen Iran, in dai ba Malami ba da yake sa rawani, don haka sai suka ce duk sojoji a rika musu wani irin aski. Sai suna musu wani aski a gewaye kai a bar gashi a tsakiyar kan. Su mutane suna zuwa ne da ‘shirt’ da wando, soja na dirowa yace ya zama nasu in ya cire ‘uniform’ sai su bashi ‘shirt’ sai ya zama dan gari.

To shine sai suka ce yanzu duk soja ya yi aski ta yadda za a gane shi, da anga wani soja ya zama dan gari sai a harbe shi. To da samarin (masu Muzahara) suka ji hakan sai kowa ya yi irin askin soja. Ko soja ya diro yanzu kansa iri daya da na mutanen gari, ba wani bambanci. Yana dirowa kawai daga mota sai a bashi ‘shirt’ da wando ya saka, ya cire bot ya sa takalmi kawai ya zama mutamin gari.

To, wannan ya daure musu kai. Sai (a ga) soja kawai ya fara kuka ya shiga cikin mutane. Sai suna mamakin wai wane irin abu ne wannan? Sai Imam ya dauki mataki wanda ba a saba ana daukan irin wannan matakin a yi nasara ba, amma sai a ga ya yi nasara.

Shi Huyser a littafinsa yana cewa wai, “rai goma yanzu zai yi maganin rai 100 nan gaba.” Ya yi ta maimaita wannan. Wato a kashe rai 10 yanzu maimakon a kashe 100 nan gaba. Ya yi ‘justifying’ kashe mutane da suke yi, domin kashe su yanzu kadan za a kashe, in aka kyale su za su yi karfin da dole sai an kashe da yawa. Kai kace ‘the only thing’ da za su yi kawai shi ne duk mai ra’ayin ‘revolution’ su kashe shi. To kuma abin ya girma, in ma kana ganin daidaiku ne yanzu ya zama sai dai in za ka kashe al’ummar gaba daya, sai ka mallaki itatuwa.

To sai ya zama suna mamakin wai wane irin mutum ne wannan? (Imam kenan). An yi an yi ya ƙi ‘confromise’ kawai, yana ta cewa lallai kawai kasa kasarsu ce, Amurka ta fita abar musu kasarsu kawai!

To har ma da kisa ya yi yawa, sai Imam Khomaini yace shi ma zai zo, ga shi nan zai zo a hada har da shi a kashe. To, wannan cewa zai koma Tehran, abin ya firgitasu.

Suka yi ‘meeting’ a kan ya za a yi ne? Wasu suka ce a hana shi sauka a filin jirgin saman Tehran, sai dai ya sauka a wani waje. Aka ce mutanensa ba za su yarda ba, za a yi rigima. Wasu suka ce a rufe ‘airpot’. Aka ce ba zai rufu ba ai.

Har ma a lokacin mutane suka fara cewa to da can muna ‘confromise’, amma yanzu in kuka hana Imam dawowa za mu fito da bindiga. To, sun san dama akwai bindigogi, amma ba a yi harbi ba, kuma a lokacin ko ba komai dama sojoji da yawa sun balle.

To, ana cikin wannan ma sai aka ce ma’aikatan ‘airforce’ da yawa sun balle. Soja kana iya samun wanda bai yi makaranta ba ya je ya yi soja, amma da ka ji an ce ‘airforce’ dole wanda ya yi karatu ne yake aikin, sojan sama wasa ne? ka san dole kasan kan gadon jirgi ko? Ba kawai za a ce maka kai sojan jirgin sama ne alhali baka sani ba. Kafin ka zama sojan sama dole sai ka yi karatu.

Saboda haka sojojin jirgin sama a cikin ‘military’ su suka fi ilimi, don su wayayyu ne, ‘minimum qualification’ din da za ka zama sojan sama dole ilimi ne mai zurfi. Sabanin zama ‘ordinary soldier/Army’ wanda yake kila ko firamare ka yi ko sakandire, ko ma a da ko baka iya rubutu da karatu ba kana iya yi, amma banda ‘airforce’.

To su ‘airforce’ a wannan lokacin suka sallama, sai suka je suka yi mubayi’a kawai, suka ce sun bi. Sai ya zama Shah ya rasa ‘airforce’. Saboda haka sai ya nemi sojan kasa su far wa ‘airforce’.

Shah ya taba sa ‘curfew’ (dokar hana fita), tun Imam Khomaini yana Paris. Kun san yadda ake ‘curfew’, a nan kasar suna yi suce sun hana kowa fita. To nan ma sun yi haukar da ba mu taba ji ba a duk duniya, sun saka ‘24 hours curfew’. A tarihin bil’adama ban taba jin an yi dokar hana fita na awa 24 ba, sai a Nigeriya da yake mahaukata ne. Wai kuma gwamnatin da aka zaba ne take wannan abin. Wai ‘24 hours curfew’ wannan hauka har ina? ‘The biggest’ hauka!

To, shi ne Shah ya saka ‘curfew’, yace daga 4 na yamma zuwa 12 na tsakar rana ba fita, wato ya ba da damar fita na awa hudu kenan a rana kawai, ka fito karfe 12 na rana, ka koma gida karfe 4 na yamma sai kuma gobe. Ba a taba jin irin wannan dokar ba a Iran kafin wannan lokacin.

Lokacin Imam yana Paris, da ya samu labarin (an saka dokar), sai yace to kar mutane su bi wannan dokar! Sai ya zama don biyayya ga Imam ba ma wanda ya kwana a gida. Ba batun ‘curfew’ ba, a kan titi mutane suka fito suna kwana. Lokacin kuma ana sanyi, amma mutane kowa ya fito ya kwana a titi.

To, lokacin da Shah ya so ‘Army’ su je su far wa ‘Airforce’, sai ya zama ba ta yadda za su bi, don mutane ne a kan titian. Kuma ‘Airforce’ din da mutanen gari suka je suka fafata da Army din, dole aka mai da su aka aje su a bariki.

Kama-kama ana nan dai al’amari ya zama dole suka bari Imam Khomaini ya koma. Kuma aka masa gagarumar tariya, irin tariyan da ba a san irinsa ba a tarihin da muka sani izuwa yanzu. Na’am, an san Manzon Allah (S) ya shiga Madina da gagarumar tariya, ana ‘dala’ar Dadaru alaina min saniyatil wada’i.’

Kuma Annabi Isa Almasihu (AS) ya shiga birnin Qudus a kan jaki, wanda aka rika masa waka, wanda aka ce har wasu Malaman gari suna cewa ka ji abin da mutane ke cewa? Ka hana su fadi, sai duwatsun gari su ma suka amsa.

To an ga tariya irin wannan wanda yake akwai a Bible, Isaiah ya fadi cewa an nuna masa mahayin jaki da mahayin rakumi, to mahayin rakumin shine Annabi Muhammad (S), don da rakumi ya shiga Madina. To ban sani ba ko Isaiah an nuna masa mahayin jirgin sama ba? (Dariya). Kila ya ga wani ya sauka a jirgin sama, ya ga tariya gagaruma. Domin shi Imam Khomaini a jirgin sama ya sauka.

Wani abin mamaki dangane da halin da ake ciki din nan, ana zaman dar-dar, jirgi ya dago daga Paris kuma ba a san abin da zai faru ba, shin za su harbi jirgin ne, ko za su hana shi sauka ne? Me zai faru? Duk mutane na firgice. Wani yace, da ya ji ance jirgin Imam ya taso firgita ya yi, yace ya za a yi ne yanzu Imam yana sama?

Amma aka ce Imam yana hawa jirgi, ya je ya zauna wajen ‘first class’ din nan, dama nan suka samar masa. Yana hawa kawai sai ya kwanta ya yi bacci abinsa. A natse kawai shi yake. Haka nan ya sauka akai gagarumar tariya.

Na takaice muku labari, domin kafin dawowar Imam kusan komai ya tsaya a Iran ma baki daya, mutane sun tsai da komai, masu sai da kalanzir sun ki sayarwa, masu kwashe shara ba kawai kwashe sharan ne basu yi ba, sun ma zuba sharan ne a hanya, ko ina biji-biji, komai ya tsaya cak! Amma da aka ce Imam zai dawo, to ko lomar tuwonka ne ya fadi a kan kwalta kana iya dauka ka ci abinka, saboda tsaftace muhalli da aka yi. Aka sa sabulu da soso aka wanke tituna, ko ina fes, aka doddora fulawowi.

Gagarumar tariya wanda aka ce a lokacin jama’ar da suka tare shi sun kai kimanin mutum miliyan shida. Wasu hotuna suna nan, wasu ‘black and white’ wasu ‘colored’, za ka ga gagarumar tariyar da akai ma Imam (QS).

Da ya sauka, farkon saukansa ya yi nufin daga nan ya wuce Bahijti Zahra ne, makabartan da aka bizne Shahidan da akai ta kashewa. Saboda haka hanyar ta gagara biyuwa daga ‘Airport’ zuwa Bahijti Zahra, saboda dafifin mutane, kowa yana son idonsa ya hango Imam.

Wasu don zari ma har sun hau kan motar da yake ciki ne ma suka zauna, da kyar ake hango Imam. Mutane dandazon mutane, titi ya cika da mutane ba zai yiwu motar tai tafiya ba. Karshe aka ga mota ba za ta tafi ba, mutane sun yi dafifi an rasa yadda za a yi da su. Saboda haka akai tunanin sai dai a zo da ‘helicopter’. Aka yi ta Koran mutane aka samu ‘space’ da kyar sannan aka zo da ‘helicopter’ ya hau ya tafi.

Ko da ya je can ma in da zai sauka ya gagara, saboda mutane suna ta cewa ina Imam zai je? Aka fada musu. A guje mutane suka kama hanyar Bahijti Zahra. Sun je sun cika ko ina yaba-yaba, aka rasa inda ‘helicopter’ zai sauka. Akai ta Koran mutane, wasu suka cire ‘belt’ dinsu suna ta juya shi haka, har aka samu wajen da ‘helicopter’ zai sauka.

Sannan kuma Imam a jawabinsa na farko ya yi wasu jawabai irin dai yadda ya saba. Yana cewa; “Haba Kanar, Haba Major, Haba Janaral, yanzu ka yarda ka zama bawan wasu kasa ka rika kashe mutanenka?”

Kuma lokacin ma gwamnatin Shah tana nan ya dawo. Sun yi yunkurin cewa ma za su kai hari a inda Imam yake, a wannan lokacin ne kuma ya zama lallai al’amari ya zama fafatawa sosai, aka jera kwana 10 cur, tun daga 1 ga watan Febrairu 1979 har zuwa 11 ga wata, kwana goma cur a jere fafatawa ne kawai ake yi, harbi kawai kake ji.

Zuwa ranar 11 ga watan Febrairu an yi ‘declairing’ karshen mulkin Shahanci da kuma tabbatar Daular Musulunci. Don haka ne ma suke kiran wadannan kwanaki goma din da ‘layalul ashr’ (10 days of layalil ashr). Wato daga 1 zuwa 10 ga watan Febrairu (da aka yi ta fafatawa), ranar 11 ga wata aka ayyana gwamnatin Shah ta tafi.”

— Bangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a yayin taron tunawa da Imam Khumain (QS) da aka gudanar a Husainiyya Baqiyyatullah Zariya a shekarar 2014.

@SZakzakyOffice
03/06/2023

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

An Yi Biki Sauƙar Al’ƙur’ani Karo Na 13 A Kano

Published

on

Harkar Musulunci a Nigeria ƙarƙashin Jogarancin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ta yi gaggarumin taron bikin saukar Al’ƙur’ani mai girma karo na 13.

Taron an yi shi ne a ranar 17 ga watan Mayu wanda yayi dai-dai da 10 ga watan Zul-Qada a cikin garin Kano, wanda ya samu a dadlin mahaddata 348 daga wasu ba’adin fudiyoyin harka da ke faɗin Nigeria da suka sauƙe ƙur’ani.

An gudanar da taron ne a ƙofar gidan Sarkin Kano, tare da halartar manya manyan baki daga garuruwa da dama.

Ga wasu hotuna na taron….

Continue Reading

Labarai

Sheikh Zakzaky (H) Ya Gana Da Daliban Fudiya Masu Shirin Yin Sauƙar Alƙur’ani

Published

on

Kamar yadda shafin ofishin Jagoran (H) ya fitar da wasu hutuna dake nuna cewa; Ɗalibai daga makarantun fudiyya daban daban dake shirin bikin hardace Alkur’ani sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), a jiya Laraba 15 ga watan May 2024 wanda yayi dai-dai da 7 ga watan Zul-Qada 1445 a gidansa dake Abuja

Ga Hotuna….

Continue Reading

Labarai

Sheikh Zakzaky (H) Ya Dawo Gida Nigeria Bayan Halartar Taro A Iraƙi

Published

on

Kamar yadda shafin Jagora (H) ya sanya wasu hotuna da yake ɗauke da saƙon dawowar shehin Malamin gida Nigeria a ranar Lahadi 12 ga watan Mayu 2024.

Shafin ya wallafa cewa; Jagoran ya dawo gida ne bayan halartar taron ƙasa da ƙasa na nuna goyon baya ga al’ummar Palastinu, wanda ya gudana a birnin Bagadaza, kasar Iraƙi a ranar Laraba 08 ga watan Mayu 2024.

Continue Reading

Trending

Copyright © 2019 By Institute for Compilation and Publication of Sheikh Zakzaky's Works.