Connect with us

Labarai

Muzahararorin Quds 2023/1444 A Nijeriya

Published

on

Fiye da garuruwa 50 ne suke gabatar da Muzaharar Quds a wannan shekarar ta 1444H/2023 a Nijeriya.

Muzaharar wacce, ake gudanar da ita a kowace Juma’ar karshen watan Ramadan, tun bayan fatawar Imam Khumaini (QS) a kan haka a shekarar 1979, inda ya yi kira ga daukar Juma’ar karshen watan Ramadan a matsayin ranar da duk al’ummar Musulmin duniya za su hadu wajen fitowa su bayyana goyon bayansu ga raunanan al’ummar Palasdinu da Yahudawan Sahayoniya suke zalunta a kokarinsu na mamaye yankin da kafa haramtacciyar kasar isra’ila.

A Nijeriya, tun a shekarar 1984 Harkar Musulunci a karkashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky take gudanarwa, a tsawon wadannan shekaru kusan 40 din, Muzaharar nuna goyon bayan Palasdinawan na kara habaka ne a kowace shekara, inda a farko ana yi ne a birnin Zariya kawai, daga baya aka koma yi a wasu birane kimanin 20 a fadin kasar, inda a yanzu a kan gudanar a birni da kauyuka fiye da 50, duk a ranar Juma’ar karshen Ramadan din.

Izuwa yanzu, wakilanmu daga garuruwa sun fara aiko mana da rahotonnin yadda Muzaharar tasu ta kasance. Gasu nan tafe a kasa:

 

1- ABUJA

Daga Ali Sajjad Tahir

Dubun dubatan ‘yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky ne suka fito Muzaharar Quds a ranar Juma’a 23 ga Ramadan, 1444 (14/4/2023) a birnin Abuja.

Muzaharar, wacce aka fara ta da misalin karfe 2 na rana daga masallacin Juma’ar Costom da ke Wuse Zone 3 a tsakiyar Abuja, ta kunshi ‘yan uwa maza da mata daga sassa daban-daban na kasar Nijeriya.

Fara muzaharar ke da wuya gamayyar jami’an tsaron ‘yan sanda da na soja suka fara bude mata wuta, amma cikin taimakon Allah ‘yan uwan suka dake suka cigaba da tafiya suna kabbarori tare da maimaita kalmar #FreePalestine.

Duk da harbe-harben da jami’an tsaro suka rika yi, muzaharar bata tsaya ba sai da ta je Beger, a yayin da ‘yan uwa suka raba musu hankali, tsiraru suka fuskanci waki’ar, mafi yawa kuma suka cigaba da muzaharar.

Izuwa yanzu muna da tabbacin an samu Shahidi guda daya, mai suna Shahid Yaqoub Umar, da kuma adadin wadanda aka raunata, sakamakon harbin da jami’an tsaron suka kara yi bayan an kammala muzaharar.

          Ga wasu daga hotunan da muka dauka:

 

2- KADUNA

Daga Muhammad Rabil

A garin Kaduna ma, ‘yan uwa sun fito Muzaharar Quds din, wadda aka faro ta da misalign karfe 2 na rana daga titin Kano Road, aka bi titin Ibrahim Taiwo Road, sannan aka isa Bakin Dogo, inda a nan ne wakilin ‘yan uwa na Kaduna, Malam Aliyu Tirmizi ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

Sai dai ana fara Muzaharar, a daidai shataletalen Leventis da ke Kaduna,  jami’an ‘yan sanda suka bude wuta akan masu muzaharar, suka raunata wasu kwarorin ‘yan uwa. Sai dai hakan bai sa Muzaharar ta tsaya ba, sai da aka kaita inda aka tsara rufe ta.

          Ga wasu daga hotunan da muka dauka yayin Muzaharar:

 

3- BAUCHI:

Daga Nusaiba Ahmad

Dubun dubatan al’ummar Musulmi ne suka fito Muzaharar ta Quds a ranar Juma’a 23 ga Ramadan, 1444 (14/4/2023) a garin Bauchi.

Muzaharar ta faro ne a Fudiyyah da ke unguwar Shagari da misalin karfe 9:23 na safiya, inda ta bi hanyar bariki, ta zagaya ta shatale-talen kofar fada, ta mike babbar hanyar titin wunti, daga nan ta shiga ta titin tashar babiye, ta bi ta bakin kura, ta shiga kofa sannan ta zagayo ta yi burki a masallacin Ajiya da ke tsakiyar garin Bauchi.

An kammala Muzaharar da misalin karfe 11:30ns, inda wakilin ‘yan uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na Bauchi, Malam Ahmad Yusuf Yashi ya gabatar da jawabin rufewa.

Muzaharar garin Bauchi ta samu halartan ‘yan uwa daga garuruwan yankin Bauchi da dama, da suka hada da Liman Katagum, Alkaleri, Kafin Madaki, Ningi, Soro, Giyade, Kyangyare, Warji, Gubi da sauransu.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar Bauchi:

 

 

4- SOKOTO

Daga Halidu Shahid Usman

A garin Sokoto, muzaharar ta fara ne da misalin karfe 9 na safiya da masallacin Alhazai da ke bayan City Campus, ta biyo ta shataletalen Diploma, ta shiga unguwar rogo, daga nan ta isa Mabera, inda aka rufe ta a wajen gidan Shahid Qasim Umar Sokoto.

Dubun-dubatan ‘yan’uwa daga garuruwan yankin Sokoto da Kebbi da Zamfara ne suka halarci Muzaharar. A bana, al’ummar garin na Sokoto sun rika yabawa da Muzaharar, ba kamar yadda aka saba a baya inda su kan rika kokarin cutar da ‘yan uwa idan sun fito ba.

Wakilin ‘yan uwa na Sokoto, Shaikh Sidi Munir ne ya gabatar da jawabin rufewa. Daga nan aka kona tutar Amurka da ta haramtacciyar kasar isra’ila.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar Sakkwato:

 

5- NGURU

Daga Abubakar Abdullahi

Da misalin karfe 8:15 na safiya aka fara Muzaharar Quds a garin Nguru da ke jihar Yobe, inda dubban ‘yan uwa daga garuruwan Bambori, Garbi, Dogon Jeji, Dumur da sauransu suka halarta.

Muzaharar ta faro ne daga titin Kwamared Bashir Sharrif, ta bi ta layin FMC, aka mike titin masallacin FK, aka miko bakin kasuwa, aka bi ta layin Gimba, daga nan aka yi kwana a daidai shataletalen Mr. Lass aka mike zuwa babban masallaci da ke kofar Fadar Nguru aka rufe ta.

Wakilin ‘yan uwa na Da’irar Nguru, Malam Aliyu Saleh ne ya yi jawabin rufewa.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar Nguru:

 

6- MASHI

Daga Salahudden Bello Sheme

A garin Mashi ta jihar Katsina ma, ‘yan uwa Musulmin daga garuruwan Mani, Maduru, Doro, Mashi da sauransu sun fito Muzaharar Quds da safiyar ranar Juma’a 23 ga Ramadan 1444.

Muzaharar wacce aka fara ta daga Markaz din ‘yan uwa na Mashi da ke sabon layi da misalin karfe 8:20 na safiya, ta mike ta hau titin Mani, ta bi ta sabon titi ta shiga unguwar kashe-naira, sannan ta dawo ta kan babban titin Katsina/Daura, inda ta isa bayan gidan NEPA da ke rijiyar alkali kusa da kotu, aka rufe ta a nan da misalin karfe 9:30ns.

Daruruwan ‘yan’uwa maza da mata ne, dauke da tutoci da banoni da suke alamta dalilin fitowarsu Muzaharar suka gudanar da ita. A yayin da wakilin ‘yan uwa na Da’irar Doro, Malam Abdulkadir Nunu ya gabatar da jawabin rufewa. Sannan Malam Sadisu Abdullahi ya yi addu’ar rufewa.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar Mashi:

 

7- AZARE

Daga Lawal Bala

A garin Azare ta jihar Bauchi, an fara Muzaharar ne bayan sallar Juma’a, da misalin karfe 2:26 na rana.

Bayan tashinta daga babban masallaci na kofar Fada, sai aka bi ta titin Sule Katagum, aka bi layin hedikwatan ‘yan sanda, sannan aka shiga layin Babani Dun Buran, aka shigo ta unguwar tsakuwa, sannan aka dawo ta kofar gari, inda aka rufe ta Sule Katagum Road da ke Azaren.

Muzaharar ta kunshi ‘yan uwa daga Da’irorin Azare, Zaki, Gamawa, Misau, Zabi, Zadawa, Giade, Shira, Yana, Jama’are, Itas, Gadau, Raga, Udubo da sauransu.

Malam Sa’id Aliyu ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

Ga wasu daga hotunan da muka dauka:

 

8- POTISKUM

Daga Ibrahim El-Tafsir

Dubban ‘yan uwa almajiran Shaikh Zakzaky na yankin Potiskum, wadanda suka hada ‘yan uwa daga Da’irorin Potiskum, Gashua, Jaji Maji, Damaturu, Fika, Gadaka, Nafada, Dambam, Dagauda, Bulkacuwa, Dawasa da sauransu, su ma sun fito Muzaharar Quds a wannan rana, domin nuna goyon bayansu ga raunanan al’ummar Palasdinu.

An faro Muzaharar ne daga makarantar Fudiyya Potiskum, inda zagayen Muzaharar ya karade kusan duk manyan titunan cikin garin Potiskum, a karshe aka rufe ta a filin wasa na Government Day Potiskum.

‘Yan uwa reras a cikin sahu, dauke da tutocin Palasdin, da banoni da kuma fastoci na #FreePalestine da #ReleaseShaikhZakzakysPassport, a yayin da mawakan Harka Islamiyya ke tafe suna raira wakokin ‘yanto masallacin Quds mai alfarma.

Duk da yanayi na rashin lafiya da wakilin ‘yan uwa na Potiskum. Malam Ibrahim Lawal yake ciki, ya samu halartar Muzaharar. Sai dai Malam Musa Fika ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

          Ga wasu daga hotunan Muzaharar:

 

9- LAFIA

Daga Saleh Haruna Nass

A garin Lafia ta jihar Nasarawa ma, almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky sun bi sahun sauran al’ummar duniya wajen gudanar da Muzaharar Allah wadai da zaluncin isra’ila a kan Palasdinawa a yau Juma’a 23 ga Ramadan 1444.

Da misalin karfe 2:33 na rana bayan kammala sallar Juma’a, ‘yan uwan da suka fito daga Da’irorin yankin Lafia kamar Doma, Agyaragu, Nasarawn Eggon, Makurdi, Azara, Shendam, Yelwa Shandam da Akwanga, suka fara gudanar da Muzaharar daga masallacin Gabas da ke hanyar Makurdi, aka bi ta babban titi, aka zagayo ta hanyar Doma, sannan aka dawo aka rufe ta a kofar sarkin Lafiyan Bare-bari.

Walikin ‘yan uwa na Lafia, Malam Muhammad Nura ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

Ga wasu daga hotunan da muka dauka:

 

10- KATSINA

Daga Bin Yaqoub Katsina

Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky na Katsina da kewaye su ma sun gudanar da Muzaharar ta Quds a ranar Juma’a 23 ga Ramadan 1444.

An fara Muzaharar ne daga babban masallacin Juma’ar Katsina, da misalin karfe 2:18 na rana, jim kadan bayan idar da sallar Juma’ar. Daga nan aka nufi Mobile, aka isa shataletalen tsohuwar tasha, aka shiga sabon layi, sannan aka bi ta kerau, daga nan kuma aka isa tsohon filin wasanni na Katsina inda aka rufe ta a nan.

Muzaharar ta kunshi ‘yan uwa daga Da’irorin Katsina, Charanci, Rimi, Abukur, Jibiya, Kudan Daga, Dutsen Safe, Kwarin Tama, Shinkafi Kaita, Kayauki, da sauransu, inda kuma ta shafe kusan awa biyu tana gudana kafin a rufe ta. Wakilin ‘yan uwa na Katsina, Shaikh Yakubu Yahya ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar:

 

 

11- ZARIYA

Daga Ali Ibrahim Yareema

A garin Zariya ta jihar Kaduna ma, dubun-dubatan ‘yan uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky ne suka fito Muzahar ta Quds a ranar Juma’a.

An fara Muzaharar ne daga masallacin Juma’a na Gwargwaje da misalin karfe 2:30 na rana, inda ta bi ta kofar Kuyan Bana, ta ratso kasuwar Zariya, ta taho zuwa Babban Dodo, inda aka rufe ta a nan.

‘Yan uwa daga yankin Zariya da suka hado Da’irorin Funtua, Kudan, Kidandan, Soba, Zariya da sauransu ne suka gudanar da Muzaharar, wacce ta shafe kusan awa daya da rabi kafin a rufe ta, inda wakilin ‘yan uwa na Zariya, Shaikh Abdulhamid Bello ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar:

 

12- GOMBE

Daga Nasir Miji

Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky na yankin Gombe ma sun gudanar da Muzaharar ta Quds, wadda ta aka faro ta daga babban masallacin Juma’a na kofar sarkin Gombe jim kafan bayan idar da sallar Juma’a.

Da misalin karfe 2:30 na rana ne aka fara Muzaharar, wanda dubban ‘yan uwa daga Da’irorin Bajoga, Dukku, Kwadon, Kumo, Filiya, Lakum, Pindiga, Talasse, Fikayel da sauransu ne suka halarta. ‘Yan uwan sun rika tafiya suna raira taken nufin ‘yanto masallacin Quds daga hannun Yahudawan sahayoniya, da kuma kira ga gwamnatin Nijeriya kan ta sakewa Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenah Ibrahim fasfo dinsu, domin su fita kasar waje neman lafiya.

Muzaharar ta samu ado da tutocin Palasdinu, inda aka rika jan tutocin Amurka da ta isra’ila a kasa, sannan kuma da hotunan Jagora da na iyalansa gami da na Shuhada masu girma. Daga masallacin Juma’a ta mike ne zuwa shataletalen cikin gari, sannan ta mike ta titin sabon layi, ta shiga ta kasuwa ta fito ta Idi, inda aka rufe ta a nan.

Wakilin ‘yan uwa na Gombe, Shaikh Muhammad Adamu Abbare ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar da misalin karfe 4:30 na yamma.

Ga wasu daga hotunan da muka samu:

 

13- KANO

Daga Muhammad Hadi (Jadda)

A birnin Kano ma, almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky sun gabatar da Muzaharar ta Quds a ranar Juma’ar, inda aka faro ta daga masallacin Juma’a na Fagge, aka bi ta titin Wafa, aka bi ta titin Katsina Road ta isa shataletalen Hajj Camp, daga nan aka juya aka bi da ita ta kofar Mazugal inda ta isa filin Dalar Gyada aka rufe ta a muhallin.

Muzaharar ta Kano, kamar sauran garuruwa, ta kunshi nuna goyon bayan al’ummar Palasdinu da kuma kira ga gwamnatin Nijeriya kan ta baiwa Shaikh Zakzaky da mai dakinsa Malama Zeenah ‘Passport’ dinsu, don su samu damar fita waje neman lafiya.

Muzaharar ta kunshi dubun-dubatan ‘yan uwa daga ‘zones’ takwas din da ke yankin Kano, wadanda suka hada da Kura, da Birnin Kudu, da Gumel, da Gwarzo, Durbunde, da Ringim da sauransu. Wakilin ‘yan uwa na Kano, Dakta Sunusi Abdulkadir ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

Ga hotunan da muka dauko:

 

14- DANDUME

Daga Haidar Mahmud, da Nazifi Ayuba

A garin Dandume ta jihar Katsina ma, ‘yan uwa sun gabatar da Muzaharar ta Quds da safiyar wannan ranar.

Muzaharar wadda ta kunshi maza da mata rike da hotuna da banoni gami da tutocin Palasdinu da na kira ga gwamnatin Nijeriya ta saki ‘Passport’ din Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenah, ta taso ne daga makarantar Fudiyyar Dandume ta hau titin Abdu Yaro, ta nufi shataletalen babban titin cikin gari, daga nan ta karade lungu da sakon garin, ta dawo bayan asibitin kasuwar mata inda aka rufe ta a nan.

Wakilin ‘yan uwa na Dandume, Malam Abdullahi Khamis ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar. Inda bayan kammala jawabinsa, aka kona tutar Amurka da ta isra’ila, sannan aka yi addu’a aka sallami jama’a.

Ga wasu daga hotunan da muka dauka:

 

15- JOS

Daga Ibrahim M. Tahir

Su ma ‘yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na garin Jos ba a bar su a baya ba, a wannan Juma’ar ta karshen watan Ramadan 1444, sun bi sahun al’ummar duniya, wajen fitowa Muzaharar nuna goyon bayansu ga raunanan al’ummar Palasdinu, da kuma yin Allah wadai da haramtacciyar kasar isra’ila da ke kashe Palasdinawa tun fiye da shekaru 80 da suka wuce.

Muzaharar ta garin Jos, wacce ta kunshi ‘yan uwa daga Da’irorin yankin Jos, kamar Rinji, Barikin Ladi, Gumau, Jos da sauransu, ta faro ne da misalin karfe 2:15 na rana, bayan idar da sallar Juma’a a babban masallacin Juma’ar Jos, inda aka faro ta daga ‘yan dankali aka gangara ta cikin kasuwar New Market aka bulla babban titin Bauchi Road, sannan aka shiga ta layin sarki, aka sake dawowa ta layin mangoro inda ta isa bakin babban masallacin Juma’a da ke tsakiyar garin.

Wakilin ‘yan uwa na Jos, Shaikh Adamu Tsoho Ahmad ne ya gabatar da jawabin rufe Muzahar.

Ga wasu daga hotunan da muka dauko:

 

16- SAMINAKA

Daga Ibrahim Almustapha

A garin Saminaka ta jihar Kaduna ma, ‘yan uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) sun gudanar da Muzaharar Quds don nuna goyon baya ga raunanan al’ummar Palasdinu da isra’ila ke zalunta, a ranar Juma’a 23 ga Ramadan 1444H.

Muzaharar wadda ta kunshi ‘yan uwa daga Da’irorin yankin Saminaka da suka hada da Lere, Ramin Kura, Garu, Mariri, Agaji, Kayarda da sauransu, ta fara ne da misalin karfe 3:00 na rana daga Fudiyyar hayin gada, inda ta miko babban titin garin, bayan shafe kusan awa biyu ana tafiya, ta iso cikin tashar mota (‘yan katako) inda aka rufe ta a nan.

Bayan isowarta muhallin rufewa, an gudanar da wakokin neman ‘yancin Palasdinawa, da kuma kira ga gwamnatin Nijeriya kan ta saki ‘Passport’ din Shaikh Ibraheem Zakzaky da matarsa Malama Zeenah don su fita waje neman lafiya. Daga bisani, wakilin ‘yan uwa na Da’irar Saminaka, Shaikh Yusuf Abubakar ya gabatar da jawabin rufewa.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar:

 

17- YOLA

Daga Shafi’u Saleh

A garin Yola, babban birnin jihar Adamawa, ‘yan uwa musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky sun bi sahun al’ummar duniya, wajen gudanar da Muzaharar Allah wadai da mamayar haramtacciyar kasar isra’ila ga al’ummar Palasdinu.

Muzaharar wadda aka fara ta da misalin karfe 2:25 na ranar Juma’a, da gudana cikin kwanciyar hankali da lumana, duk da tsananin zafin rana da kuma azumi da ake yi.

An fara Muzaharar ne daga babban masallacin Juma’a na Nasarawo, aka ratsa babban titin Muhammad Mustapha, aka bi ta bakin kasuwar Jimeta aka komo ta hanyar Zaranda street, sannan aka ratsa titin Wukari street inda aka rufe ta a kofar shiga makarantan Sakandiren gwamnatin jihar (Capital School).

Malam Usman Sa’ad ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar. Inda bayan nan aka kona tutar Amurka da isra’ila kurmus, sannan aka gabatar da Malam Dalhatu Musa ya rufe da addu’a.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar da muka samu a shafin Adamawa Press Team:

 

18- GUSAU

Daga Lawal Maigari

Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a garin Gusau ta jihar Zamfara ma sun gudanar da Muzaharar ta Quds a ranar Juma’ar karshen Ramadan.

An fara Muzaharar ne da misalin karfe 3:20 na rana daga Masallacin Kanwuri, inda aka bi titin gidan sarki, aka hau hanyar tsohuwar kasuwa, daga nan aka isar da ita shataletalen Bello Barau aka rufe ta.

‘Yan uwa daga Da’irorin Kauran Namoda, Tsafe, Talatar Mafara da Gusau ne suka halarci Muzaharar, wadda Malam Shu’aibu S. Kaya ya gabatar da jawabin rufe ta, Malam Sada Muhammad Ladan kuma ya yi addu’ar rufewa.

Ga wasu daga hotunan Muzaharar:

 

 

19- BIRNIN KEBBI

Daga Alhussaini Nasir

A Birnin Kebbi ma, almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky sun jagoranci Muzaharar ta Quds don nuna goyon baya ga al’ummar Palasdinu a ranar Juma’a 23 ga Ramadan, 1444.

Muzaharar wacce ta kunshi ‘yan uwa daga Da’irorin yankin Kebbi da suka hada Gwandu, Jega, Andarai, Gwadangaji da sauransu, an fara ta ne bayan idar da sallar Juma’a daga babban masallacin Juma’a na garkar sarki da ke cikin Birnin Kebbi, inda aka bi da ita babban titin tsakiyar gari, a karshe aka rufe ta a shataletalen Rabin Atiku.

Wakilin ‘yan uwa na Birnin Kebbi, Malam Umar Bello ne ya gabatar da jawabin rufe Muzaharar.

Ga wasu daga hotunan yadda Muzaharar ta gudana:

 

Za mu cigaba da dorawa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Muzaharar Goyon Bayan Palasdinawa A Kaduna; An Samu Shahidai 2

Published

on

Da misalin karfe 11 na safiyar Ranar Alhamis 16/11/2023 (2/5/1445) ‘yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a Kaduna, suka fita Muzaharar nuna goyon baya ga raunanan al’ummar Palasdinawa da Yahudawan Isra’ila ke kashewa.

Muzaharar wacce ta kunshi mata da kananan yara, an faro ta ne daga Nepa Roundabout da ke tsakiyar garin Kaduna, ta isa gaban ofishin Hukumar kare hakkin ɗan Adam (Human Right Commission), sai ga jami’an ‘yan sandan Mopol nan, suna zuwa suka fara bude wuta, da harbi da bindiga da Tiyagas, inda suka jikkata gomomin ‘yan uwa, a yayin da biyu daga ciki zuwa yanzu suka cika sakamakon harbin.

Shahidan su ne; Shahid Sidi Anas Kaduna, wanda matashi ne dan kimanin shekaru 30, yana da mata da yarinya daya, sai kuma Shahid Muhsin Abubakar, wanda shi yaro ne dan kimanin shekaru 15 da haihuwa.

A yayin Muzaharar, yan uwa mata sun rike abubuwan da ke alamta jariran Palasdinawa da Isra’ila ke kashewa a tsakanin nan, musamman a hare-haren da Haramtacciyar ƙasar isra’ila din ke kaiwa a yankin Gaza a asibitoci, makarantu da gidajen al’umma, wanda yau kimanin kwanaki 40 kenan ana cikin wannan halin.

Ga wasu daga hotunan da wakilinmu Muhammad Rabil ya turo mana na yadda Muzaharar ta gudana.

— Cibiyar Wallafa Da Yada Ayyukan Shaikh Zakzaky (H)

Tuntuba: cibiyarwallafa@gmil.com

Website: www.cibiyarwallafa.org

#FreePalestine

#PalestinianLivesMatter

#PalestineWillBeFree

Continue Reading

Labarai

Takaitaccen Tarihin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

Published

on

An haifi Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), a unguwar Kwarbai da ke cikin garin Zaria ta jihar Kaduna a ranar 15 ga Sha’aban 1372 Hijiriyya (Miladiyya: 28 April, 1953).

Mahaifinsa shi ne Malam Yaqoub, dan Malam Ali, dan Sharif Tajuddeen, dan Liman Husaini, wanda asalinsu tsatson Manzon Allah Muhammad (S) ne, ta hanyar Imam Hasanul Mujtaba (AS), wanda suka iso kasar Hausa daga garin Shingidi da ke tsohuwar daular Mali ta da.

KARATUN ALKUR’ANI DA LITTATAFAI A ZAURUKAN MALAMAN ZAZZAU

Bayan tasowar Shaikh Zakzaky, ya yi karatun littattafan addini a wajen Malamai daban-daban a garin Zazzau. Ya fara da karatun Alkur’ani a wajen mahaifinsa, da kuma karatun wani littafin Fiqihun Malikiyya mai suna ‘Jiddil Aaziz’ a wajen kakarsa Haajar (da ake kiranta Maikaratu).

Ya kuma cigaba da karatun Alkur’ani (na Allo) a gidan Sarkin Ladanan Zauzzau na lokacin, da kuma wajen Malam Sani Abdulkadir, wanda shi bayan karatun Alkur’ani ya rika hada musu da littafan Fiqihun Malikiyya da kuma Larabci. Banda karatun bai-daya, Shaikh Zakzaky ya rika saka littattafai a gaban Malam Sani Abdulkadir, inda ya sauke littafai irinsu Akhdari, Ishmawi, ‘Dan-Rushdi, ‘Dan-Ashir, Qurdabi, Badamasi, ‘Ya Dalibal Li’irabi, Mulha, Ajruma, Rubu’iyya da sauransu, wadanda duk littafan Fiqihu ne da na Lugga a kasar Hausa a wancan lokacin.

Shaikh Zakzaky (H) ya kuma cigaba da karatu a zauren wani Malami mai suna Malam Isa Na Madaka, inda ya biya littafai masu yawa a gabansa, daga ciki akwai littafin ‘Ta’alimi’, da littafan Iziyyah da Risala, wadanda su littafan Fiqihun Malikiyya ne, da Alburda wanda shi yabon Manzon Allah (S) ne cikin harshen Larabci. Sannan kuma ya kammala karatun Risala, ya yi littafin Askari da Wardi da wasu littafan a gaban Malam Sani Na’ibin Zazzau.

Shaikh Zakzaky, ya kuma yi karatu a wajen Malam Ibrahim Na Kakaki, a wajensa ya kammala littafin ‘Askari’ da ‘Mukhtasar’ da wani littafin Nahwu mai suna ‘Saja’i’, da ‘Alfiyar Dan Maliki’ da ‘Makamatul Hariri’ da wasu littafan Lugan Larabci da Nahwu da dama.

KARATUN NIZAMIYYA A ZARIYA DA KANO

A shekarar 1969, lokacin Shaikh Zakzaky yana dan shekaru 16 da haihuwa, a sannan ya sauke Alkur’ani mai girma, ya kuma sauke mafi yawan littafan Fiqihu da Luga da ake yi a zaurukan Malaman Zazzau a lokacin, sai ya shiga wata makarantar Nizamiyya mai suna “Provincial Arabic School” a Zariya, inda ya yi ta tsawon shekara biyu, ya kammala a 1971.

Bayan ya ci jarabawar wannan makarantar ne ya samu damar zuwa makarantar horar da Malamai ta “School for Arabic Studies” wadda aka fi sani da SAS a Kano, inda ya yi ta daga 1971 zuwa 1975 ya kammala da kyakkyawan sakamako. Da yake ita makarantar SAS ana tarbiyar Malamai ne don su je su koyar a mataki mafi inganci a makarantu a bangaren Larabci da addini, don haka an fi karfafa karatun addini a cikinta.

Sai ya kasance akwai wasu darussan ‘Advance Level’, da mutum yake da zabi ya jona su da karatunsa, sai ya rika zuwa ana musu ‘lesson’ dinsu da yamma (wato ba a ainihin lokacin makarantar ba). Kuma mutum na iya zana jarabawar shiga Jami’a daga wannan ‘Advance level’ din. Sai Shaikh Zakzaky, bisa zabin kansa ya jona da ‘Advance level’ din, inda ya karanta English literature, Economics, Government, Hausa, Arabiyya da kuma Islamic studies. Bayan kammala ta a 1975 kuma ya zana jarabawar ‘Grade II Certificate’, da kuma na ‘Advance Level’ din, duk ya ci su, wannan ya bashi damar shiga Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zariya kai tsaye.

KARATUN LITTATAFAI A ZAURUKAN MALAMAI A KANO

Tsawon shekaru hudun da Shaikh Zakzaky ya yi yana karatun Nizamiyya a Kano, ya kuma rika hadawa da zuwa zaurukan Malamai daban-daban yana cigaba da karatun Littattafan addini da Luggan Larabci.

Ya yi karatu a wajen wani Malami Baqadire mai suna Malam Shawish Abdallah, a unguwar Sagagi, inda a wajensa Shaikh Zakzaky ya sake yin bita da maimaicin da yawa daga littafan da ya biya su tun a gida (Zazzau). Da yake Malam Shawish almajirin Malam Yusuf Makwarari ne, shi kuma Almajirin Sheikh Nasiru Kabara (shugaban dariqar Kadiriyya na Afirka a lokacin), don haka ta wajensa Sheikh Zakzaky ya rika zuwa gidan Sheikh Nasiru Kabara, inda sukan saurari karatun Tafsirin Alkur’ani da kuma littafin Ashafa da yake gabatarwa.

Sannan kuma, akwai Malam Isa (wanda daga baya ya zama Wazirin Kano), yana daga cikin Malaman da suke koyarwa a SAS a lokacin, don haka, Shaikh Zakzaky ya rika karatun littafai a kebe a wajensa, inda ya biya littafai da dama, daga ciki akwai wani littafi mai suna ‘Hukkami’ na Malam Zaqqaqi, wanda yake sharhi ne na ‘Matnil Ghasimiyyah’. Sannan ya karanta ‘Tajridus Sarih’, wanda littafi ne da aka takaice maimaicin Hadisan cikin Sahihul Bukhari, aka yi shi cikin mujalladi biyu.

Har ila yau, a karshen shekarar 1973 bayan Shaikh Zakzaky ya koma zama a unguwar Yola da ke cikin Birnin Kano, ya rika karatu a gaban limamin unguwar Yolan, mai suna Malam Nuhu. Shima a wajensa Sheikh ya maimaita wasu littafan da ya yi a baya ne, irin su ‘Askari’, ‘Muktasar’, ‘Alfiya’ da ‘Makamatul Hariri’.

KARATUN JAMI’A DA FARA DA’AWA

Bayan shigan Shaikh Zakzaky jami’ar Ahmadu Bello (ABU) a shekarar 1976, sai ya tarar da wasu yanayoyi na sako-sako da addini ga dalibai da malamai Musulmin da suke Jami’ar, da kuma yadda ya ga bangaren Kiristoci da masu ra’ayin Kwaminasanci suna hujumi ga addinin Musulunci da kokarin nuna shi a mummunan kama, da ma yadda aka wayi gari baro-baro nizamin da ke mulkin kasar na fada da addinin Musulunci. Ganin wadannan yanayoyin ya sa Shaikh Zakzaky ya fara Da’awar a komawa tsarin Musulunci, wanda ya shafe shekaru uku yana kiran a asirce (a cikin jami’o’in kasar kawai), kafin bayyana da’awar a fili ga al’umma a shekarar 1980.

Tun a watan Disambar 1976 da aka yi wani taron IVC na dalibai Musulmi a garin Gombe, Shaikh Zakzaky ya fara bijiro da bukatar a tattauna dangane da me ya kamata ya zama makomar a kasar nan, ganin cewa ana yayin ra’ayin Kwaminisanci a tsakanin daliban jami’a a lokacin. Ya bijiro da tambaya a tsakanin dalibai Musulmi (MSS), inda a karshe ya bar mutane su je su yi tunani da kansu ba tare da ya fada musu shi abin da yake ganin shi ne mafitan a tashin farko kai tsaye ba. Har zuwa sadda aka hadu a IVC din gaba, sannan fitar musu da hakikar abin da yake nufi.

A IVC na gaba, wanda aka yi a watan Afrilun 1977 a Katsina, nan ne Shaikh Zakzaky ya bayyanawa dalibai Musulmi ra’ayinsa kan cewa, lallai fa ba abin da ya dace ya tafi da rayuwar Musulmi da al’amuran kasar da Musulmi ne mafi rinjayenta kamar tsarin addinin Musulunci. A nan ne ya kirkiri wani bangare da ya saka ma suna ‘External Enlightenment Division’ (EED), inda ya bukaci duk mai sha’awa ya ba da sunansa, saboda za su rika zama bayan kammala kowane taron IVC na MSS, suna karatun addini da kwakkwafe fikirar Musulunci. Daga nan ne masomin Da’awar Harkar Musulunci.

Sai ya zama duk lokacin taron IVC Shaikh Zakzaky kan shirya lakcar musamman don kwakkwafe fikirar Musulmi. Sannan kuma bayan gama taron IVC sukan kara kwanaki tare da mambobin wannan EED din, suna karatun littafan da ke koyar da Fikirar addini da tarbiyar ruhi. Har ya zama an samu wasu daidaiku da suka ji a ransu suna shirye su sallama rayuwarsu a kan kira zuwa ga komawa tafarkin Allah.

A shekarar 1979, wadda ita ce shekarar karshe na karatun Shaikh Zakzaky a jami’ar ABU, suna ma cikin jarabawar karshe, sai wani abu ya faru, wanda ‘yan kungiyar shan giyan kwakwa suka rika amfani da muhalli, da kwanuka, da ababen amfanin Musulmi wajen shan giyarsu, inda su Shaikh Zakzaky suka bi duk matakan da ya dace na kai karansu ga hukumar jami’ar, amma ta ki hana su, don haka, sai su Shaikh suka hana su da karfi, suka farfasa giyan nasu, suka tarwatsa su a wajen.

Wannan abin da ya faru, sai ya jawo hankalin ba kawai hukumar jami’ar ba, har ma fadar Shugaban kasa na lokacin, Olusegun Obasanjo, inda ta turo jami’an tsaro aka girke su a kofar jami’ar, bisa goyon bayanta da ba da kariya ga mashaya giyan. Kuma aka kama Shaikh Zakzaky da gomomin Musulmin kungiyar MSS aka tsare, sai bayan kwanaki aka sake su bisa wani tsararren beli, sannan kuma aka kori wadanda suke rike da mukaman MSS a daidai lokacin daga jami’ar.

Wannan abin ya saka wa Shaikh Zakzaky tunani a kan cewa, ashe duk barnar da ake yi a kasar shi nizamin da ke tafiyar da kasar ne ya ke goyon bayansa, kuma shi ke turo (barnar) cikin al’umma ma. Kuma sai ya zama bayan an sake su, an sake yi musu jarabawar da basu yi ba (sakamakon kama su da aka yin), kuma shi (Shaikh) ya ci jarabawar da kyakkyawan sakamako, amma hukumar makarantar ta ki ta ba shi sakamakonsa sam. Don haka, a lokacin sai Shaikh ya muhimmanta cigaba da da’awarsa na kira zuwa ga komawa addinin Allah (T), da kawar da tsari, ko nizamin da ya sabawa na Allah Ta’ala gabadaya.

SHELANTA DA’AWAR HARKAR MUSULUNCI

A watan Junairu zuwa Febrairun 1980 ne, Shaikh Zakzaky ya samu halartan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a karo na farko, a karkashin kungiyar Dalibai Musulmi na kasa (MSS), wanda a lokacin shi ne mataimakin shugaban kungiyar bangaren harkokin kasashen waje. Wannan ziyarar da Shaikh Zakzaky ya kai Iran, ya shafe kusan makonni biyu a can, inda ya dawo a wajajen ranar 14 ga Febrairun 1980 din. Kuma a yayin wannan ziyarar Shaikh Zakzaky ya samu tagomashin ganawada Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Imam Ruhullah al-Khomeini (QS), inda Imam din ya yi musu jawabi, kuma har Shaikh Zakzaky ya dauko a kaset ya yi tsaraba da shi.

Bayan dawowar Shaikh Zakzaky daga Iran, ya rika shirya lakcoci a manyan jami’o’in kasar nan, da suka hada da Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU), Jami’ar Jos, jami’ar Lagos, Jami’ar Bayero Kano (BUK), Jami’ar Sokoto da sauransu, inda ya rika ba da labari a kan abubuwan da ya gani a jamhuriyyar Musulunci ta Iran a yayin  ziyararsa. Tare da kunna kaset din jawabin Imam Khomaini da ya dauko yana bayani don isar da sakon addini.

A ranar 5 ga watan Afrilun 1980 kuma, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fara shelanta da’awan kira zuwa ga tafarkin Allah a gaban dandazon al’ummar Musulmi a garin Funtua (wadda a yanzu take jihar Katsina). Al’amarin da aka ambace shi da ‘Shelar Funtua’ ko “Funtua Declaration” a Turance.

Duk da cewa Shaikh Ibraheem Zakzaky ba yana matsayin dalibi ba ne a wannan lokacin, amma dai shi ne mataimakin shugaban kungiyar dalibai Musulmi na kasa (MSS), a wannan taron da kungiyar ta gabatar a Funtua, Shaikh Zakzaky sai ya wakilci shugaban kungiyar na lokacin, Ahmad Falaki wanda bai samu halarta ba. Sai Shaikh ya yi amfani da wannan damar, ya karanta wani jawabi da a ciki yake bayyana tawaye ga duk wani tsari da ya sabawa na Allah (T), ya kuma bayyana goyon bayansa ga Allah (T) da shari’arsa, ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi tawaye ga tsarin mulkin kasar wanda ya yi hannun riga da tsarin Allah (T), tare da kiran mutane kan su zo a hadu a yi yunkurin tabbatar da addini da shari’ar Allah (T) na Alkur’ani a kasar nan.

HARE-HAREN MAHUKUNTAN NIJERIYA GA SHAIKH ZAKZAKY

Wannan shelar da Shaikh Zakzaky ya yi, ta karbu a cikin al’ummar Musulmin Nijeriya, wannan yasa nan da nan hukumar kasar ta fara kokarin kawar da shi da da’awar tasa, ta hanyar kamu, da afkawa, da kuma kisa ma a wasu lokutan, kamar haka;

1- Gwamnatin Alhaji Shehu Shagari, ta kama Shaikh Zakzaky (H) da ‘yan uwa uku a ranar 15 ga Afrilun 1981, lokacin da suka je taron IVC na dalibai Musulmi a Sokoto, inda bayan tsare su da aka yi a Kurkukun Sakkwato na tsawon watanni 5, a watan Satumbar 1981 aka kawo musu waranti cewa kotu ta daure Shaikh Zakzaky shekaru 4 bisa laifin yin wa’azi ba tare da lasisi ba, sauran mutum ukun kuma shekaru biyu-biyu. Sai a ranar 15 ga Afrilun 1984, bayan shafe shekaru uku cur a tsare a kurkukun Inugu sannan Allah ya kaddara fitowar Shaikh Zakzaky.

2- A farko-farkon watan Disambar 1984 din, Janaral Muhammadu Buhari ya hambare gwamnatin Shehu Shagari, a wannan watan kuma ya kama Shaikh Zakzaky ya tsare shi a Interrogation Center da ke Lagos na tsawon watanni uku, tun daga Disambar nan har zuwa watan Maris 1985, bayan haka, sai suka mai da Shaikh din kurkukun Kiri-kiri inda ya shafe watanni biyar a can yana tsare. Har ya zama an haifa wa Shaikh Zakzaky yaronsa na farko mai suna Muhammad, lokacin yana tsare a wannan kamun ne. Sai a farkon watan Satumbar 1985 bayan Babangida ya hambare gwamnatin Buhari sannan ya saki Shaikh Zakzaky.

3- A Ranar Asabar 28 ga watan Maris 1987, sai shi ma Janaral Ibrahim Badamasi Babangida ya kama Shaikh Ibraheem Zakzaky, tare da matarsa da wasu ‘yan uwa maza da mata, a lokacin matar tana da cikin ‘yarsa ta biyu mai suna Nusaibah, don haka ba ta jima ba suka sake ta. Shi kuwa Shaikh Zakzaky sun tsare shi a kurkukun Kaduna na tsawon watanni takwas, sannan suka mayar da shi kurkukun Fatakwal suka tsare shi har zuwa ranar 28 ga watan Nuwambar 1989 Allah Ya nufi fitowarsa, bayan shafe shekaru kusan uku a tsare.

4- A karo na biyu a mulkin Janaral Badamasi Babangida, a watan Nuwambar 1991 jami’an tsaron farin kaya suka kama Shaikh Ibraheem Zakzaky a filin jirgin saman Aminu Kano, daidai lokacin zai je taro a London. Inda suka tsare shi a ofishinsu da ke Kano na kwana daya, kashegari suka tafi da shi hedikwatansu da ke Lagos, suka tsare shi kusan kwanaki hudu da sunan bincike, daga karshe Allah ya kubutar da shi a wannan lokacin aka sake shi.

5- A ranar Alhamis 12 ga watan Satumbar 1996, Janaral Sani Abacha ya turo jami’an tsaro har gida suka kama Sheikh Ibraheem Zakzaky suka tafi da shi Kaduna, suka tsare a hedikwatan ‘yan sanda. Kashegari Juma’a da ‘yan uwa suka fito Muzaharar kira a saki Malaminsu, sai jam’an tsaro suka bude wuta a daidai kofar Doka a garin Zariya, nan take suka kashe mutum 15, suka ji wa gomomi rauni. Bayan kwanaki biyu da kama su Shaikh, ranar Asabar, suka kai shi kurkukun Fatakwal (Port Harcourt) babban birnin jihar River, suka tsare shi tsawon watanni tara a can, sai a ranar 2/6/1997, suka dawo da shi kurkukun Kaduna suka cigaba da tsare shi har zuwa ranar 18 ga Disamba 1998, bayan shafe shekaru biyu da kusan rabi yana tsare sannan suka sake shi. A lokacin an kama Shaikh tare da wasu ‘yan uwa, bayan kamun kuma an cigaba da kama ‘yan uwa a fadin kasar, tare da cigaba da budewa almajiransa wuta a lokutan Muzaharori da tarurruka a tsawon mulkin Abacha da lokacin rikon kwaryan Abdussalami Abubakar.

6- A ranar 14 ga Disambar 2015 sojojin Nijeriya bisa umurnin shugaban kasa Muhammadu Buhari suka sake kama Shaikh Ibraheem Zakzaky, bayan sun kwana biyu suna bude wuta a kan almajiransa a gidansa da ke Gyallesu da kuma Husainiyyah Bakiyatullah da Darur Rahma, inda suka kashe kusan mutum dubu. Bayan sun kashe ‘ya’yansa a gabansa, sun harbi matarsa da shi kansa, suka kama shi suka tafi da shi cikin jini, suka tsare a wajen jami’an tsaron farin kaya (DSS) a Abuja da Kaduna, daga karshe suka mai da shi da matarsa kurkukun Kaduna. Sai a ranar 28 ga watan July, 2021, bayan shafe kimanin shekaru shida da rabi ana tsare da su, sannan kotu ta wanke su daga dukkan tuhumomin da gwamnati ke musu, ta sake su ba tare da wani sharadi ba.

7- A tsawon wadannan shekaru kusan 45 na Da’awar Harkar Musulunci, gwamnatin Nijeriya ta rika kai hare-hare daban-daban a lokuta daban-daban a kan almajiran Shaikh Zakzaky (H), tun tana amfani da ‘yan tauri da masarautun gargajiya, ta koma amfani da ‘yan Izala (Wahabiya), ta koma fitowa kai tsaye ta bude wuta ta hanyar jami’an tsaronta. A yayin da ta sha yunkurin kashe Shaikh Zakzaky a lokuta daban-daban, daga ciki akwai lokacin fitina Tawayiyya inda suka yi manyan yunkuri har karo biyu; karo na farko a cikin masallacin BUK, karo na biyu a makarantar Technical, da kuma lokacin Shugaban kasa Alhaji Umar Musa ‘Yar’adua, da suka yi nufin jefa bom a gidan Shaikh Zakzaky, shi ma Allah Ta’ala ya kare. Da kuma lokacin Goodluck Ebele Jonathan da suka yi gomomin yunkurin kai wa Shaikh Zakzaky hari a gidansa da daddare ko a kan hanyar zuwansa Husainiyyah a ranakun zuwa bayar da karatu.

MALAMAN SHAIKH ZAKZAKY NA IMAMIYYAH

Tun zuwan Shaikh Zakzaky jamhuriyar Musulunci ta Iran a shekarar 1980, ya dawo da tsarabar wasu daga littafan Imamiyya, irin su “al-Istibsar” da “Attahzib” na Shaikh Dusi, da “al-Mabsud”, da littafan su Shaikhud Da’ifa, da na Muhaqqiqul Hilli (RH) da sauransu, tunda yana da shimfidar karatun gida, ya rika bitansu a kan kansa a lokutan da yake tsare a kurkukun da aka rika kama shi a wannan tsakanin. In an lura, tsakanin shekara goman 1980 zuwa 1990 Shaikh Zakzaky ya shafe shekaru kusan bakwai ne a tsare a kurkuku daban-daban.

Har zuwa shekarar 1990, da ya fara zuwa karatu a Hauza Ilmiyyah da ke Ghana, inda ya rika karatu a wajen wani Malami mai suna Sayyid Tabataba’I, wanda a lokacin ya zo Afirka da nufin Tablig (isar da sakon addini), musamman sun bi littafin Biharul Anwar da wasu littafan suna bahasinsu. Tsawon kimanin shekaru uku, duk karshen wata Shaikh Zakzaky kan je ya yi kwanaki ya dawo.

Bayan haka kuma, ba jimawa da fitowarsa daga Kurkukun kamun Abacha, sai ya fara zuwa Daura Ilmiyyah a jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana karatu a wajen Malamai daban-daban. Daga cikinsu akwai Shaikh Jaafarul Hadi, wanda ya karantar da Shaikh Zakzaky fannoni daban-daban, musamman Aqida, da kuma Usul.

Ya kuma yi bahasi dangane da littafin Nahjul Balgaha na Amirulmuminin (AS) gabadayansa a wajen wani Malami mai suna Shaikh Suwaidi. Wannan ya faru ne tun kafin Shaikh din ya fara karantar da littafin Nahjul Balagha. Da kuma Farfesa Dahiri, wanda Sheikh Zakzaky ya yi karatun Mandiq a wajensa. Sannan ya karanci Tafsirin Alkur’ani, inda suka bi Tafsirin Ayatullah Jawadi Amuliy (Tasneem fi Tafsirul Qur’an) da wani Malami wanda shi yana daga cikin jigon aikin tarjamawa da rubuta Tafsirin a lokacin, mai suna Shaikh Haaqani.

Tun ana kan tarjama shi zuwa Larabci, kafin a kai ga bugawa suka yi bitansa. Kila wannan ya taimaka wajen sanyawa Shaikh Zakzaky tasiri, inda a wani lokaci a farkon gabatar da Tafsirinsa zagaye na uku, ya bayyana cewa, hatta Tafsirin Alkur’ani yana bukatar Taqalidi, saboda haka, shi ya dauki Ayatullah Jawadi Amuli a matsayin Marj’insa a bangaren Tafsirin Alkur’ani.

Har ila yau, cikin Malaman da suka karantar da Shaikh Zakzaky, akwai Sheikh Tabasi da ke Qum, da kuma Ayatullah Ahmadi, da Sheikh Munzir Hakeem, da Sayyid Ridawiy da sauransu.

Duk lokacin da Sheikh Zakzaky ya je wannan Dauran Karatun a Iran, yakan shafe kimanin kwanaki 40 ne a can yana karatun kafin ya dawo, yakan je kusan duk shekara ko bayan watanni, tun wajajen shekarar 2000 har zuwa shekarar 2015 kafin Waki’ar Buhari ta Zariya.

KARANTARWARSA

Shaikh Ibraheem Zakzaky ya rika karantar da Tafsirin Alkur’ani da kuma wasu littafai, tun a shekarunsa na Jami’a, musamman kuma daga shekarar 1980 bayan shelanta da’awa, ya fara karantar da almajiransa Tafsirin Alkur’ani, inda suke karantarsa tare da aikata shi kai tsaye. Wadanda suka shaidi farkon Harkar nan, sun bayyana cewa, a wancan lokacin, idan aka karanta Aya daya, da Allah Ta’ala ke umurni da a yi sallar dare, sai a tsaya a ga an tsayu da sallar daren kafin a cigaba da dauko wasu Ayoyin ana bitansu. Idan aka karanta Ayar da Allah Ta’ala Ya yi umurni ga Annabi (S) akan ya gargadi mutane, sai a tashi a je cikin gari a rika tunatar da mutane a kan manufar Allah Ta’ala na yin Dan Adam a doron kasa, da bukatuwa zuwa ga komawa tsarin Allah da shari’a da Alkur’ani.

Da yake an rika kama Shaikh Zakzaky ya shafe shekaru a Kurkuku, hatta a Kurkukun, Shaikh Zakzaky ya rika karantar da mutane daban-daban littafan addini idan suka nuna sha’awa, ko kuma idan ya zama kamun ya hada da ‘yan uwa, kamar kamun Waki’ar Kafancan (na lokacin Babangida), wanda Shaikh din ya rika koyar da ‘yan uwa karatun Alkur’ani da Tafsirinsa. Haka ma a lokacin kamun Abacha, bayan dawo da su kurkukun Kaduna, ya rika karantar da almajiransa da suke tare da shi littafan addini, irin su littafin Tahrirul Wasila na Imam Khomaini, da littafan Alkhlaq da na Aqida da sauransu.

Bayan mallakar Fudiyyah Islamic Center a Zariya a shekarar 2002, Shaikh Zakzaky ya fara gabatar da Tafsirin Alkur’ani, inda kowa da kowa ke iya halarta a duk ranar Laraba a tsawon shekara, a yayin da idan Ramadan ya zo, sai a koma yi kullum, har ya zama an sauke Tafsirul Mubin a karon farko tare da sirkawa da ruwayoyi daga littafan Ahlis Sunnah, saboda kokarin fahimtar da mutanen da ake tare da su.

Bayan haka, Shaikh ya sake dauko Tafsirin a karo na biyu, tare da takaita bayanai, har zuwa sadda aka shiga Suratul Ahzab, sannan ya fara fadada bayanai da karanto ruwayoyi daga A’immatu Ahlulbaiti (AS) dangane da ma’anar Ayoyi. Bayan an yi sauka na biyu, a yayin da aka faro sauka karo na uku kuwa, sai ya zama gabadaya Tafsirin ana yinsa ne daga littafan Tafsiran Imamiyya, tare da fassara kowace Aya da ruwayoyin da aka samu daga A’imma (AS) dangane da fassararsu. Sai dai ana cikin Suratul Aali Imran ne, aka yi waki’ar Buhari a 2015, wanda zuwa yanzu ba a cigaba ba.

Har ila yau, Shaikh Zakzaky ya rika karantar da littafin Nahjul Balagha a duk ranar Litini a Fudiyyah Islamic Center, har zuwa shekarar 2010 bayan an samu Husainiyyah Bakiyyatullah, karatun ya dawo nan.

Baya ga wannan, Shaikh Zakzaky na karantar da wasu daga almajiransa karatuttuka kebantacce (Khaas), inda sukan shafe wata guda suna gabatarwa, kusan kowace shekara sau biyu. Daga darussan da yake basu akwai bangaren Fiqihu, da Aqida da Akhlaq. A yayin da kuma duk ranar Talata yake zama tare da ‘yan uwa mata, suma yana karantar da su ilmummukan addini daban-daban, zaman da aka fi sani da ‘Majlis’.

KAMMALAWA

A yanzu haka, Shaikh Ibraheem Zakzaky yana da shekaru 73 a Hijiriyya, a Miladiyya kuma kimanin shekaru 70 kenan. Matarsa daya ce, Malama Zeenah Ibrahim, sun haifi ‘ya’ya tara (9) da ita; maza 7, mata 2. Mutum shida daga cikin ‘ya’yan nashi, Allah Ta’ala Ya azurta su da samun Shahada; uku daga cikinsu; Ahmad, Hamid da Mahmud, sun yi shahada a lokacin Waki’ar Muzaharar Quds ta 2014, sai kuma Hammad, Ali da Humaid, wadanda sojoji suka kashe su a gaban mahaifansu a lokacin da suka kawo hari a gidan Shaikh din a shekarar 2015.

Yanzu akwai Nusaiba da Suhaila a raye, sai kuma babban yaron Shaikh Zakzaky, mai suna Muhammad, wanda yake da mata daya da yara biyu; Husain (Naadir) da kuma kanwarsa Naseemah (Fatimah).

 

Wallafawa:   Cibiyar Wallafa Da Yada Ayyukan Shaikh Zakzaky (H).

Tuntuba:      cibiyarwallafa@gmail.com

Website:       www.cibiyarwallafa.org

Facebook:    www.facebook.com/cibiyarwallafa2016

Continue Reading

Labarai

Jami’ar Tehran Ta Karrama Jagora Shaikh Zakzaky Da Digirin Girmamawa

Published

on

A yammacin ranar Asabar 29 ga Rabiul Auwal 1445 (14/10/2023), Jami’ar Tehran (Tehran University), da ke Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ta shirya gagarumin biki don karrama Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) da Digirin Girmamawa.

Jami’ar, ta bai wa Shaikh Ibraheem Zakzaky Digirin Girmamawan ne a bangaren Ilimin Nazarin Duniya, Zaman Lafiya da Warware Rikici (World Studies: Peace and Conflict Resolution).

Da yake jawabi a wajen taron, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya bayyana cewa, ya sadaukar da wannan shaidar ta Doktora ga daliban Harkar Musulunci a Nijeriya da suke karatu a Iran, da kuma ga al’ummar Nijeriya bakidaya.

A shekarar 2020 ma, wata Jami’a a kasar Iraqi ta taba baiwa Shaikh Zakzaky Digirin Girmamawa, a daidai lokacin da yake tsare a kurkukun Buhari.

Shaikh Ibraheem Zakzaky da matarsa Malama Zeenah sun isa birnin Tehran da ke Jamhuriyar Musulunci ta Iran a ranar Laraba 11/10/2023 da nufin samun damar ganin kwararrun likitoci don duba lafiyarsu daga jinyar da suka shafe shekaru takwas suna fama da, tun bayan harin sojojin Nijeriya a kansu a karshen shekarar 2015.

A safiyar ranar Asabar din ne, Shaikh Zakzaky da iyalansa suka gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci, Ayatollah Sayyid Khamenie a gidansa da ke birnin Tehran. A yayin da ake da ran Shaikh Zakzaky da tawagarsa za su wuce garin Masshad a ranar Lahadi 15/10/2023, don jinyar da ya kai su.

Ga wasu daga hotunan da muka samu daga kafafen yada labarai daban-daban na yadda bikin ya gudana:

Continue Reading

Trending

Copyright © 2019 By Institute for Compilation and Publication of Sheikh Zakzaky's Works.